Gwamnatin jihar Katsina Ta Shirya Taron Majalisar Kasa Na 17 Akan Muhalli

top-news

Katsina Times 

 A shirye shiryen karbar bakuncin taron Majalisar Ƙasa kan Muhalli  karo na 17 da ke tafe, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda PhD, ya kafa wani kwamiti mai mambobi 11 na Local Organising Committee (LOC).  

Taron wanda aka shirya gudanarwa tsakanin ranakun 11 zuwa 16 ga watan Disamba, 2023, ana sa ran zai samu wakilai da mahalarta daga sassan kasar.

 Kwamitin wanda sakataren gwamnatin jihar Barista Abdullahi Garba Faskari ya kaddamar, an dora mashi muhimman ayyuka.  Waɗannan Ayyuka sun haɗa da kai tare da Babban Kwamitin Tsarawa don tabbatar da adadin masu halarta, samar da masaukin da suka dace, da kuma tsara sufuri ga mahalarta.

 A karkashin jagorancin Kwamishinan Muhalli, Alhaji Musa Adamu Funtua, Kwamitin na LOC ya kunshi fitattun mutane kamar Sakatarorin dindindin daga manyan ma’aikatun da suka hada da Muhalli, Noma da Dabbobi, Lafiya (Tertiary Institution), Ayyuka, Gidaje da Sufuri.  
Alhaji Salisu Abdu, Alhaji Kabir Amoga, Alhaji Isa Duwan, Alhaji Lawal Abdullahi, da Nura Ibrahim daga ofishin sakataren Gwamnati ne a matsayin manyan mambobin kwamitin.

 Daga cikin muhimman ayyukanta, an wajabta wa Kwamitin na LOC da tabbatar da ingantacciyar sanarwa da matakan tsaro don samun nasarar gudanar da taron.  A yayin da shirye-shiryen ke kara gabatowa, jihar Katsina na sa ran za ta karbi bakuncin taron majalisar zartarwa na kasa kan muhalli mai a watan Disamba 2023.

NNPC Advert